Duka 'Yan Nijer Mazauna Amurka Ne Su Ka Yi Zanga-Zangar Lumana, Ko A'A?
Shugaban Nijer Mahamadou Issoufou
Wasu 'yan Nijer sun ce su duka ne suka yi zanga-zangar lumana a birnin New York, wasu kuma sun ce ba haka batun ya ke ba
WASHINGTON, DC —
Mataimakin shugaban kungiyar 'yan kasar jamahuriyar Nijer mazauna Amurka, malam Issa Gado wanda ke birnin New York ya ce a yau asabar sun yi zanga-zangar lumana a kofar ginin Majalisar Dinkin Duniya domin jan hankalin shugabannin Nijer kan matsalolin da ke addabar kasar yanzu haka:
Your browser doesn’t support HTML5
Issa Gado mataimakin shugaban kungiyar 'yan Nijer a New York.-1':32"
Amma da yake maida martani game da wannan batu na cewa duka 'yan kasar Nijer mazauna Amurka ne su ka yi zanga-zangar lumanar, malam Moutari alhaji Garba Azzarori Madaoua shugaban jam'iyar PNDS Tarayya a birnin Harrisburg, jahar Pennsylvania ya ce babu wani dan kasar Nijer mazaunin Harrisburg da ya je New York da sunan yiwa gwamnatin kasar zanga-zangar lumana:
Your browser doesn’t support HTML5
Moutari alhaji Garba Azzarori Madaoua shugaban PNDS a Harrisburg.-1':20"
Halima Djimrao ce ta tattauna da Malam Issa Gado da kuma malam Moutari alhaji Garba Azzarori Madaoua.