Najeriya Na Kashe Rabin Kudaden Shigarta Akan Biyan Bashi

Debt relief

Wani rahoto da bankin raya kasashen Afrika ya fitar ya yi nuni da cewa Najeriya na amfani da kashi 50 cikin 100 na kudaden shigarta wajen biyan kudin ruwan basussuka da ta karbo daga kasashen ketare.

Wannan rahoto na zuwa ne, a daidai lokacin da hukumomin Najeriya ke cewa suna shirin kara ciwo basussuka domin gudanar da wasu ayyuka.

A cewar Malam Yusha’u Aliyu, masani kan harkokin tattalin arziki, ba illa ba ne idan Najeriya ta karbo bashi, amma dai abu mai matukar muhimanci ne da ya kamata mahukunta su mai da hankali akan shi.

Dalar Amurka

“Gaskiya abin damuwa ne a ce kasar da take da albarkatun mai take da yawan jama’a, a ce kuma irin wannan kaso yana tafiya wajen biyan kudin bashi.”

Amma a cewar, Yusha’u, shi bashi ba matsala ba ne a karbe shi, “matsalar ita ce yanayin irin kudin ruwan da za a biya akan bashin.”

Saurari cikakken hirar Malam Yusha’au Aliyu da Mahmud Lalo.

Your browser doesn’t support HTML5

Najeriya Na Kashe Rabin Kudaden Shigarta Akan Biyan Bashi