Kamfanin dillancin labaran SANA ya bayyana cewa, gine-ginen na cikin yankunan Mazzeh da Qudsaya, da ke yammacin babban birnin kasar.
Syria-Israel
Gidan rediyon sojojin Isra'ila ya ce wuraren da aka kai harin a Damascus, hedkwatar kungiyar 'yan gwagwarmayar Falasdinawa ta Islamic Jihad ne da kuma abin da ta bayyana a matsayin wasu kadarori, ba tare da yin karin haske akai ba.
Israel-Hamas-Gaza-Faladina-Gabas ta Tsakita
Isra'ila dai ta shafe shekaru tana kai hare-hare kan wuraren da ke da alaka da Iran a Syria amma ta kara kai hare-hare tun a ranar 7 ga watan Oktoban bara bayan da kungiyar Hamas ta Falasdinu ta kai hari yankin Isra'ila wanda ya haifar da yakin Gaza.
Syria-Israel
An san kwamandojin kungiyar Hezbullah ta kasar Lebanon da dakarun Revolutionary Guards na Iran da ke Syria suna zama a Mazzeh ne, a cewar mazauna yankin da suka tsere bayan hare-haren baya-bayan nan da suka yi sanadiyar mutuwar wasu daga cikin manyan kungiyoyin.
-Reuters