Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya maka Majalisar Dokokin jihar a kotu akan ikirarinta na zargin cewar gwamnatinsa ta shekaru 8 ta wawure naira biliyan 432 inda ta bar jihar cikin dimbin bashi.
A yau laraba ne El-Rufa'i ya maka Majalisar Dokokin Kadunan a gaban babbar kotun tarayya dake jihar akan tauye masa hakkokinsa.
Tsohon gwaman Kaduna, Nasir El-Rufai
Karar wacce lauyan tsohon gwamnan, Abdulhakeem Mustapha, mai lambar Babban Lauyan Najeriya (SAN) ya shigar ta kalubalanci rahoton kwamitin majalisar wanda ya samu El-Rufa'i da laifin aikata almundahana.
Tsohon gwaman Kaduna, Nasir El-Rufai da lauyansa
A kunshin karar, El-Rufa'i ya bukaci kotun ta ayyana rahoton binciken majalisar a matsayin mara tushe kasancewar bai bashi damar kare kansa daga zarge-zargen da kwamitin ke yi masa tare da gwamnatinsa ba.
Wadanda ke cikin kunshin karar sun hada da Majalisar Dokokin Kadunan da antoni janar kuma kwamishinan shari'a na jihar.