Shugaban Amurka Joe Biden ya yi alkawarin ba da tallafin dala biliyan hudu domin a kara kaimi wajen samar da allurar rigakafin cutar COVID-19 ga kasashe marasa galihu.
An saki jerin sunayen wakokin da za su fito a sabon fim din "Coming To America 2" da ake shirin haskawa a watan Maris.
Muna taya sabuwar shugabar WTO, Okonjo-Iweala, murna.
Tsohon mataimakain shugaban Najeriya kuma dan takarar mukamin shugaban kasa karkashin babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya, ya soki matakin kama masu zanga zanga da aka yi.
Kasashen Nahiyar Afurka da sauran kasashe marasa karfi sai su sha kuruminsu, ga mai share musu hawayensu.
Tsohon dan wasan Chelsea Diego Costa na shirin kulla yarjejeniyar shekara biyu da kungiyar kwallon kafa ta Palmeiras da ke Brazil, wacce ya kasance yana kauna tun yana yaro.
Shahararren mawakin kudancin Najeriya Peter Okoye, wanda aka fi sani da Mr. P. ya nuna bacin ransa kan fadan kabilancin da ya faru a Ibadan babban birnin jihar Oyo.
Majalisar Dattawan Amurka, ta wanke Donald Trump a yunkurin tsige shi da aka yi a karo na biyu cikin shekara guda, inda ‘yan Republican suka hana a dora masa laifi mummunan harin da magoya bayansa suka kai a ginin majalisar dokokin kasar.
Tun bayan da aka fara zanga zanga a Myanmar kan juyin mulkin da sojoji suka yi, ma’aikatan lafiya sun bi sahun masu wannan bore wajen nuna adawarsu da matakin sojin.
Kungiyar kwallon kafa ta Burnley a gasar Premier ta Ingila, ta bi Crystal Palace har gida ta lallasa ta da ci 3-0.
Ana sa ran a ranar Asabar, sanatoci a majalisar dattawan Amurka za su saurari muhawarar karshe kan shari’ar tsige tsohon shugaba Donald Trump.
Dan wasan Manchester United wanda har ila yau yake bugawa kasar Ingila kwallo, Marcus Rashford, ya ce magance matsalar cin zarafi a kafafen sada zumunta “abu ne mai sauki.”
Fitacciyar jarumar masana’antar Kannywood a arewacin Najeriya, Fati K.K. ta yi amarce.
Kungiyar Tampa Bay Buccaneers a Amurka, ta lashe kofin gasar NFL a wasan karshe na Super Bowl a Amurka.
Matashiyar nan da ta ja hankalin Amurkawa da wakar-baka a bikin rantsar da shugaba Joe Biden a watan da ya gabata, ta sake haskawa a wasan karshe na gasar kwallon kafar Amurka wato Super Bowl.
Hukumomi a Haiti sun ce sun dakile wani yunkurin da aka yin a kashe shugaba Jovenel Moise tare da kifar da gwamnatinsa a jiya Lahadi, yayin da ake ci gaba da kai ruwa rana kan yaushe wa’adin mulkinsa zai kare.
Manchester City ta je har Anfield ta lallasa Liverpool da ci 1-4 a gasar cin kofin Premier ta Ingila.
Wasa tsakanin Liverpool da Manchester City a gasar cin kofin Premier, ba wasa ne da ke daukan hankalin masoya kwallon kafa a kasar ta Ingila kadai ba, har ma da sauran sassan duniya yayin da kowa ya zira ido ya ga yadda wannan wasa zai karkare.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya yi lale marhabin da goyon bayan da Amurka ta nuna wa Dr. Ngozi Okonjo Iweala wacce ake fatan za a zaba a matsayin sabuwar shugabar kungiyar kasuwanci ta duniya WTO.
Domin Kari