Fitaccen mawaki Ali Jita a masana'antar Kannywood da ke arewacin Najeriya, ya ce rasuwar mahaifinsa babban rashi ne a rayuwarsa.
Tsohuwar Ministan kudin Najeriya, Ngozi Okonjo-Iweal, na shirin zama mace ta farko kuma ‘yan nahiyar afrika ta farko, da za ta shugabancin kungiyar hadahadar kasuwancin duniya WTO.
Amurka ta bayyana matakana da take shirin dauka kan juyin mulkin da aka yi a kasar Myanmar da kuma shugaban 'yan adawa a Alexie Navalny da hukumomin Rasha suka kama.
Gidan talbijin din sojin kasar Myanmar na Myawaddy, ya bayyana cewa dakarun kasar sun karbe ikon tafiyar da mulkin kasar karkashin dokar ta-baci.
Wani rahoto da aka wallafa, ya nuna cewa kwantiragin Lionel Messi a Barcelona na tsawon shekara hudu ya kai euro miliyan 555.2 ko dala miliyan 673.8.
A karshen makon da ya gabata, an samu muhimman labarai na nishadi da suka faru, kama daga bangaren wakoki na arewaci da kudancin Najeriya zuwa fannin shirya fina-finai. Ku duba, domin karanta wasu daga cikinsu.
Shugaban Amurka Joe Biden, ya kwashe makonsa na farko yana soke wasu daga cikin tsare-tsaren gwamnatin tsohon shugaban kasa Donald Trump, tare da bayyana irin matakan da gwamnatinsa za ta dauka kan wasu muhimman batutuwa kamar na COVID-19.
Manchester City ta zama club ta tara da ta zauna a saman teburin gasar Premier a wannan kakar wasa.
Kwanan nan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea da ke wasa a gasar Premier ta Ingila ta sanar da Thomas Tuchel a matsayin sabon kocin club din.
Mahaifin jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood Ibrahim Maishunku ya rasu.
Ana sa ran samar da karin allurar riga-kafin cutar COVID-19 zai taimaka wajen farfado da karfin tattalin arzikin duniya a wannan shekara, a cewar wani hasashe da hukumar ba da lumani ta IMF ta yi a ranar Talata.
Novak Djokovic da Rafael Nadal na shirin fara karawa a kakar wasa ta 2021 a gasar ATP ta Australian Open.
Fitaccen mawakin Hausa na zamani, Lilin Baba ya saki wani sabon kundi mai dauke da wakoki 14 wanda ya mai take da “Sounds From the North,” wato sautuka daga arewa.
Tsohon shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Dr. Bukola Saraki ya nuna damuwarsa kan rikicin makiyaya da manoma da ke wakana a jihohin Ondo da Oyo lamarin da har ya kai ga aka ba Fulanin wa’adin su tashi a wasu yankunan jihar ta Oyo.
Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, ta sallami mai horar da ‘yan wasanta Frank Lampard daga mukaminsa bayan da kungiyar ta tsaya a matsayi na tara a teburin gasar Premier League ta Ingila.
Shahararrun mawaka Lady Gaga da Jennifer Lopez na daga cikin mawakan da suka cashe a bikin rantsar da shugaban Amurka Joe Biden a ranar Laraba 20 ga watan Janairu.
Masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood ta tana ruwan fidda fina-finai a wani abu da masu lura da al’amuran da suka shafi harkar fim suke ganin bashi ne masana’antar take biya saboda cikas da annobar coronavirus ta haifar a bara.
Ga dukkan alamu, an yi hannun riga tsakanin Shatta Wale da Burna Boy sanadiyyar zargin gutsiri-tsoma da ya gitta tsakanin manyan mawakan biyu a karshen makon da ya gabata.
Manchester United ta ci gaba da mallake saman teburin gasar Premier League bayan da ta tashi canjaras da tsohuwar abokiyar hamayyarta Liverpool a filin wasa na Anfield.
Gwamnatin Najeriya ta ce ya zama dole a bar Rev. Matthew Hassan Kukah ya yi addininsa da siyasarsa ba tare da tsangwama ba.
Domin Kari